fidelitybank

Gini ya kashe ‘yan gida daya a Kano

Date:

Wasu yara ‘yan gida daya sun rasa rayukansu sakamakon ginin da ya rufta akansu a lokacin da suke cikin ɗaki.

Ginin ya rufto ne sakamakon mamakon ruwan sama lokacin da yaran suke bacci.

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Kano ta tabbatar da mutuwar mutum goma sha takwas sakamakon ambaliyar ruwa a sassan jihar.

Mahaifin yaran ya ce bai jima da kwanciya ba sai ya ji ƙara bayan anyi wani ruwa mai ƙarfi.

“Ƙarar da na ji ta girgiza ko ina sai na firgita na tashi, ina miƙe wa sai na ji ƙarar ƙaramar yarinyata tana hun wayyo Allah a danne ni,ina fitowa kawai sai naga bangon daƙin gaba ɗaya ya fadi a kansu.” in ji mahaifin.

“Duka yarana biyar ne a cikin daƙin daya rushe.”

Mahaifin ya ce moƙocin shi ne ya taimaka masa suka ɗaga wani katako inda suka samu suka fito da yara uku yayin da kuma aka kasa ceton sauran biyun.

Shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa na jihar Kano,Isiyaku Abudllahi Kubarachi ya ce ambaliyar ruwa a Kano ta yi sanadin mutuwar mutane da dama da kuma rushewar gine-gine.

“Waɗanda suka rasa rayukansu a wannan shekarar a ƙananan hukumominmu muna da kamar mutum 18 a yanzu inda waɗansu ɗakuna ne suka faɗa musu a ka, wasu kuma gonankinsu za su je kuma guraren da akwai ruwa kuma za su tsallaka, daga nan ne ake samun matsala.” in ji shugaban.

Shugaban ya kuma ce a cikin ƙiyasinsu gabakiɗaya dai akwai mutum 8,773 waɗanda irin wannan lamarin ya shafa a jihar Kano.

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp