fidelitybank

Gini ya kashe ‘yan gida daya a Kano

Date:

Wasu yara ‘yan gida daya sun rasa rayukansu sakamakon ginin da ya rufta akansu a lokacin da suke cikin ɗaki.

Ginin ya rufto ne sakamakon mamakon ruwan sama lokacin da yaran suke bacci.

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Kano ta tabbatar da mutuwar mutum goma sha takwas sakamakon ambaliyar ruwa a sassan jihar.

Mahaifin yaran ya ce bai jima da kwanciya ba sai ya ji ƙara bayan anyi wani ruwa mai ƙarfi.

“Ƙarar da na ji ta girgiza ko ina sai na firgita na tashi, ina miƙe wa sai na ji ƙarar ƙaramar yarinyata tana hun wayyo Allah a danne ni,ina fitowa kawai sai naga bangon daƙin gaba ɗaya ya fadi a kansu.” in ji mahaifin.

“Duka yarana biyar ne a cikin daƙin daya rushe.”

Mahaifin ya ce moƙocin shi ne ya taimaka masa suka ɗaga wani katako inda suka samu suka fito da yara uku yayin da kuma aka kasa ceton sauran biyun.

Shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa na jihar Kano,Isiyaku Abudllahi Kubarachi ya ce ambaliyar ruwa a Kano ta yi sanadin mutuwar mutane da dama da kuma rushewar gine-gine.

“Waɗanda suka rasa rayukansu a wannan shekarar a ƙananan hukumominmu muna da kamar mutum 18 a yanzu inda waɗansu ɗakuna ne suka faɗa musu a ka, wasu kuma gonankinsu za su je kuma guraren da akwai ruwa kuma za su tsallaka, daga nan ne ake samun matsala.” in ji shugaban.

Shugaban ya kuma ce a cikin ƙiyasinsu gabakiɗaya dai akwai mutum 8,773 waɗanda irin wannan lamarin ya shafa a jihar Kano.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp