fidelitybank

Gini ya kashe mutane 11 a ɗakin motsa jiki na China

Date:

Mutane 11 sun mutu bayan rufin dakin wasan motsa jiki na makaranta a arewa maso gabashin China ya rufta a lokacin da wata tawagar ‘yan wasan kwallon raga ta ‘yan mata ke amfani da shi, kamar yadda kafafen yada labarai na kasar suka ruwaito.

Da dama daga cikin wadanda lamarin ya rutsa da su kananan yara ne, kamar yadda shaidun gani da ido suka sanar da kafafen yada labaran kasar, duk da cewa har yanzu ba a tabbatar da hakan a hukumance ba. In ji BBC.

Iyayen da ke cikin rikicewa sun yi cincirindo a wani asibiti da ke kusa suna neman ƙarin bayani.

Mutane takwas ne kawai daga cikin 19 da ke cikin dakin motsa jiki a lardin Heilongjiang na masana’antu suka tsira.

Gidan rediyon kasar Sin ya bayyana cewa, an ji mai horar da ‘yan wasan kwallon raga na makarantar yana kiran sunayen daliban yayin da tawagar masu aikin ceto suka isa cikin ginin, a birnin Qiqihar don ceto rayukan yaran.

the nation newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp