Gwamna Mai Mala Buni na Yobe ya jajantawa iyalan wadanda wani masallaci da ya rufta a garin Machina da ke karamar hukumar Machina a jihar.
Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Gubana ya wakilta, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici da ban tsoro yayin da ya kai ziyarar jaje a ranar Lahadi a Machina.
Kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) ya rawaito cewa, masallacin da aka shafe kimanin shekaru hudu ana ginin, ya ruguje ne a ranar 31 ga watan Maris, inda mutane hudu suka mutu yayin da wasu 30 suka samu raunuka daban-daban.
Yayin da yake addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu, Buni ya bayyana shirin gwamnati na tallafa wa al’umma domin samun nasarar kammala aikin.
Shi ma da yake nasa jawabin, Sheikh Khalifa Fatihu ya bayyana cewa, aikin da aka tsara shi da masallaci da kuma cibiyar Musulunci, ya kaddamar da shi ne tare da goyon bayan al’ummar yankin domin tunawa da ‘Sheik Mohammad Gibirima’, mahaifinsa marigayi.
Fatihu ya yabawa gwamnatin Yobe bisa yadda ta nuna damuwa da jajircewa.
Ya roki a ci gaba da addu’ar zaman lafiya da ci gaban jihar da kasa baki daya.