Tsohon gwamnan jihar Abia kuma bulaliyar majalisar dattawa, Sanata Orji Uzor Kalu, ya bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da marawa shugaban kasa Muhammadu Buhari baya a kokarinsa na sake dawo da kasar nan.
Da ya ke karin haske game da nasarorin da shugaban kasar ya samu, tsohon gwamnan ya jaddada cewa shugaba Buhari ya himmatu wajen ganin ko da ci gaban kasar ne, ya kara da cewa farfado da ababen more rayuwa a yankin Kudu maso Gabas ba zai yi wu ba idan shugaban ya nuna son kai ga Ndigbo.
Kalu a yayin da ya ke gargadin ‘yan siyasa da su guji kalaman kyama da kamfen na zage-zage ga shugaban kasa, ya nuna cewa shugaba Buhari ya cancanci yabo daga ‘yan Najeriya ba tare da la’akari da bambancin kabila ko addini da siyasa ba.
Tsohon Gwamnan, wanda ya bayyana hakan a ranar Laraba a lokacin da ya karbi tawagar masu ruwa da tsaki na Isi Ugwu a ziyarar hadin kai a Abuja, kamar yadda mai taimaka masa a yankin Arewa, Aminu Shehu Uba Sharada ya aikewa manema labarai.
Ya ce, “Na yi farin ciki da ziyarar masu ruwa da tsaki daga Isi- Ugwu da ke karamar hukumar Ohafia ta jihar Abia. Kamar yadda ku ka ambata, ayyukan tituna da sauran ababen more rayuwa da a ke aiwatarwa a gundumar Abia ta Arewa ba za su iya yi wu ba sai da goyon bayan shugaba Buhari. Ina da kwarin gwiwa na saukaka ayyuka zuwa gundumar Abia ta Arewa, saboda goyon bayan da shugaban kasa ya ba ni”. Inji Kalu.
“Gwamnatin tarayya ta APC karkashin jagorancin shugaba Buhari ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen gina ababen more rayuwa a shiyyoyi shida na kasar nan. Shugaban kasa ya cancanci a yi mana addu’a kamar yadda Allah ya kaddara masa ya jagoranci ‘yan Nijeriya da Nijeriya.
“Littattafai masu tsarki sun jaddada cewa ya kamata mu yi wa shugabanninmu addu’a, domin haka dole ne mu kiyaye ka’idojin Littafi Mai Tsarki da Alkur’ani mai tsarki. A ko da yaushe na ci gaba da tabbatar da cewa shugaba Buhari ya na goyon bayan kungiyar Ndigbo da ma Najeriya baki daya. Idan a ka yi la’akari da ayyukan da gwamnatin tarayya ta tabbata a yankin Kudu maso Gabas da sauran sassan Najeriya, a bayyane ya ke cewa shugaban kasa ya himmatu wajen gina kasa mai albarka. Shugaban kasa dan Najeriya ne mai tsananin tawaya kuma mai kishin kasa”. Inji Kalu.
Tsohon Gwamnan ya kuma yabawa tawagar bisa wannan ziyarar, inda ya ce ba zai yi kasa a gwiwa ba wajen samar da rayuwa mai ma’ana ga al’ummar mazabar sa.