fidelitybank

Gidauniya ta za ta mayar da kai wajen koyar da wasanni da samar da ilimi a Najeriya – Dan wasan Dortumnd

Date:

Ɗanwasan ƙwallon ƙafa na ƙungiyar Dortmund da ke Jamus, Karim Adeyemi ya buɗe gidauniya a Najeriya.

Adeyemi, wanda yanzu yake wakiltar tawagar ƙasar Jamus, asalinsa ɗan Najeriya, kasancewar mahaifinsa ɗan Najeriya ne.

Ya buɗe gidauniyar ne a birnin Ibadan da ke jihar Oyo, ya ce gidauniyar za ta mayar da hankali kan koyar da wasanni da ilimi.

A kwanakin baya da ya ziyarci Najeriya, Adeyemi ya shaida wa BBC cewa nan gaba yana tunanin komawa taka leda a gasar Premier ta Ingila.

A gasar zakarun turai ta bana, ɗanwasan ya zura ƙwallo uku rigis a ragar ƙungiyar Celtic a wasan da suka fafata.

A game da gidauniyar, ya ce, “na san yadda rayuwa take a nan Najeriya da kuma yadda rayuwa take a Jamus. Na daɗe ina da tunanin idan na samu ɗaukaka ta hanyar ƙwallon ƙafa, zan koma asalina a Najeriya in taimaka wa mutane. Ba zan taɓa mantawa da asalina ba. Wannan babban abin alfahari ne,” in ji shi.

assu update

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp