Babban gida yarin Monrovia da ke Liberia ya fara daina karɓar ɗaurarun da ake turo masa saboda cikar da ya yi da kuma fargabar ɓarkewar cututtuka.
Minsitan harkokin Shari’a na Liberia Frank Musa Dean ne Ya shaida wa BBC cewar waɗanda aka ƙi karɓar su ana zargin su ne da aikata ƙananan laifuka.
“Idan ba a yi wa wani rauni ko illa ga wani ba, mutanen da aka tsare kan ƙananan laifuka, yanzu za su koma gida sai masu unguwanninsu su dinga sa ido a kansu.
Hakan dai ya biyo bayan rahotanin da wasu daga cikin kafafen yaɗa labaran kasar suka yi na yadda masu gadin gidan yarin ke ƙin amincewa da karɓar sababbin ɗaurarun, saboda yajin aikin da suke yi kan jikirin biyansu albashi.
Sai dai shugabannin gidan yarin sun musanta hakan.
An gina gidan yarin ne da zummar ɗaukar mutum 300, a lokacin da adadin mutanen Monorovia bai wuce dubu 300 ba.
Sai dai a yanzu yana dauke da mutum 1,600, yayin da adadin mutanen Monorovia ya kai miliyan daya da rabi.
Wandan ke zaune a gidan yarin sun hada da waɗanda aka yanke wa hukucin kisa da masu fashi da makami.