fidelitybank

Gidan Yarin Liberia ya daina karbar masu laifi saboda cinkoso

Date:

Babban gida yarin Monrovia da ke Liberia ya fara daina karɓar ɗaurarun da ake turo masa saboda cikar da ya yi da kuma fargabar ɓarkewar cututtuka.

Minsitan harkokin Shari’a na Liberia Frank Musa Dean ne Ya shaida wa BBC cewar waɗanda aka ƙi karɓar su ana zargin su ne da aikata ƙananan laifuka.

“Idan ba a yi wa wani rauni ko illa ga wani ba, mutanen da aka tsare kan ƙananan laifuka, yanzu za su koma gida sai masu unguwanninsu su dinga sa ido a kansu.

Hakan dai ya biyo bayan rahotanin da wasu daga cikin kafafen yaɗa labaran kasar suka yi na yadda masu gadin gidan yarin ke ƙin amincewa da karɓar sababbin ɗaurarun, saboda yajin aikin da suke yi kan jikirin biyansu albashi.

Sai dai shugabannin gidan yarin sun musanta hakan.

An gina gidan yarin ne da zummar ɗaukar mutum 300, a lokacin da adadin mutanen Monorovia bai wuce dubu 300 ba.

Sai dai a yanzu yana dauke da mutum 1,600, yayin da adadin mutanen Monorovia ya kai miliyan daya da rabi.

Wandan ke zaune a gidan yarin sun hada da waɗanda aka yanke wa hukucin kisa da masu fashi da makami.

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp