fidelitybank

Gidan tarihin Birtaniya ya dawo da wasu kayan da ya sace zuwa Najeriya

Date:

Gidan tarihin Birtaniya y mayar wa da masarautar Benin tagulla biyu, fiye da karni ɗaya da sojojin Birtaniya suka yi awon gaba da su, matakin da ake ganin zai buɗe ƙofar dawo da dubban kayayyakin tarihi zuwa asalinsu a Najeriya.

Kayayyakin da sojojin Birtaniya suka sace a 1897, yawancinsu suna gidajen tarihin ƙasashen Yammaci da kuma wasu gidajen tarihin masu zaman kansu.

Masu bincike da ƴan mulkin mallaka ne yawanci suka sace kayayyakin tarihin. In ji BBC.

Tagullan Benin da dubban kayan ƙere-ƙere na al’adu da mutum-mutumi da hauren giwa, sun kasance alamu da ake zargi na rashin adalci. Asalinsu daga yankin da ake kira jihar Edo ne a yanzu a Kudancin Najeriya.

An yi ƙasaitaccen biki na tarɓar tagullan guda biyu da aka dawo da su a masarautar Benin.

Akwai wasu da dama da ake tunanin an adana su a New Zealand da Amurka da kuma Japan.

Tun a watan Oktoba Jami’ar Aberdeen ta miƙa tagullan guda biyu ga ofishin jekadancin Najeriya.

A na tunanin akwai kashi 90 na kayayyakin tarihi na Afirka da ke gidan tarihin Turai a Faransa da kuma gidan tarihin Birtaniya na London.

Gidan tarihin Birtaniya, da ke da kayan tarihin Benin 950, ya sha suka musamman saboda ƙin amincewa ya dawo da su, amma yana ɗaya daga cikin gidajen tarihin da ke ƙoƙarin tabbatar kayayyakinsa a bisa doka.

breaking news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp