fidelitybank

Gidaje 22 ne suka rushe a Najeriya cikin wata 6 a Najeriya – COREN

Date:

Majalisar Dokokin Injiniya a Najeriya, COREN, ta ce an samu rugujewar gine-gine 22 tsakanin Janairu zuwa Yuli 2024 a ƙasar nan.

Shugaban COREN, Farfesa Sadiq Abubakar ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai ranar Laraba a Abuja.

Taron manema labarai mai taken, “Rugujewar Gine-gine a Najeriya a Kwanakin baya: Kira don Dorewar Haɗin Kai daga Duk Masu ruwa da tsaki.”

A cewar Abubakar, daga watan Janairu zuwa 14 ga watan Yuli kadai, an samu rahoton rushewar gini har sau 22 a Najeriya, inda Legas ke da kashi 27.27, Abuja da Anambra na da kashi 18.18 cikin 100 kowanne.

Ya kuma bayyana cewa Ekiti da Plateau sun biyo baya da kashi 9.09 kowanne, sannan jihohin Kano, Taraba, da Neja na da kashi 4.55 kowanne.

“Haka zalika, bayanai sun nuna cewa Legas ce ke kan gaba wajen rugujewar gine-gine.

“A gaskiya, sama da gine-gine 91 ne suka ruguje, wanda ya yi sanadiyar mutuwar sama da mutane 354 a Legas daga shekarar 2012 zuwa yau.

“Hakazalika, a Abuja, kimanin gine-gine 30 ne suka ruguje daga shekarar 1993 zuwa yau, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 64 tare da jikkata wasu da dama.

“Abubuwan da suka faru na baya-bayan nan na rushewar gini a kusa da DMGS Onitsha, Jihar Anambra, a ranar 12 ga watan Yuni da na wata makaranta (Saint Academy) da ke Filato a ranar 13 ga Yuli, inda dalibai 22 suka mutu, 134 suka jikkata, da kuma rushewar ginin a ranar 13 ga watan Yuli. Kubwa, Abuja,” ya kara da cewa.

Shugaban na COREN ya ce abubuwan da suka faru suna da ban tsoro, yana mai jaddada cewa suna kira da a zurfafa tunani da hadin gwiwa a tsakanin masu ruwa da tsaki wajen dakile bala’in.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp