fidelitybank

Ghana za ta fara tura Malaman jinya Birtaniya

Date:

Gwamnatocin Ghana da Birtaniya za su sanya hannu kan wata yarjejeniyar tura malaman jinya daga Ghana zuwa Birtaniya, wani abu da zai sanya Ghana ta samu ƙarin kuɗaɗen shiga da suka kai fan 1,000 a kan kowace malamar jinya ɗaya.

Ministan lafiya na ƙasar, Kweku-Agyeman-Manu ya shaida wa majalisar dokokin Ghana cewar “muna gab da sanya hannu kan yarjejeniyar, ciki har da waɗanda karatunsu ya tsaya a (ƙaramin) satifiket, za su je su samu horo sannan su dawo gida bayan shekara uku.”

A 2020 ma Ghana ta tura malaman jinya 100 zuwa tsibirin Barbados domin tallafa wa ƙasar wadda ke fama da ƙarancin malaman lafiya.

A baya dai shugaban Ghana Nana Akufo-Addo ya ce ƙasar na da wadatattun malaman jinya, har ma da rara, amma tura su asibitocin gwamnati na da wahala.

Sai dai shugabar ƙungiyar malaman jinya da ungo-zoma ta Ghana, Perpetual Ofori-Ampofo ta shaida wa BBC cewa ƙasar na fuskantar ƙarancin malaman jinya da za su yi aiki a asibitocin ƙasar.

Ghana na da malaman jinya masu rajista kimanin 120,000, amma kashi 46% ba su da babbar takardar karatu.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp