fidelitybank

Ghana ta soke hukuncin kisa ga masu laifi

Date:

Majalisar dokokin Ghana ta soke hukuncin kisa, bayan da amince da yin gyara ga dokar hukumar manyan laifuka ta 2022. Ya biyo bayan tsawon lokaci na hanƙoro daga kungiyoyin kare hakkin bil adama na ganin an yi watsi da dokar.

Lauya mai hanƙoron kare hakkin dan’adam kuma dan majalisa Francis-Xavier Kojo Sosu ne ya miƙa wa majalisar kudirin dokar domin sauya ta tare da goyon bayan wata kungiya da ke Birtaniya mai rajin ganin an yi watsi da hukuncin kisa (Death Penalty Project).

Ya ce “A kan hukuncin kisa, fursunoni suna farkawa da tunanin cewa wannan ita ce ranarsu ta ƙarshe a duniya. Sun kasance kamar matattu masu rai, sun daina yi kamar mutane saboda haka soke hukuncin kisa zai nuna cewa a matsayinmu na al’umma mun kuɗuri aniyar cewa ba za mu kasance masu cin mutunci ko haifar da rashin zaman lafiya ba.”

A halin yanzu akwai maza 170 da mata 6 da aka yanke wa hukuncin kisa, waɗanda a yanzu za a maye gurbin hukuncin da daurin rai da rai.

Ko da yake kotuna a Ghana sun zartar da hukuncin kisan ne kan waɗanda aka samu da laifin kisan kai da yunkurin aikata kisa da kisan kare dangi da kuma fasa-ƙwaurin zinare; ba a cika aiwatar da hukuncin ba. Ghana ta zartar da hukuncin kisa na ƙarshe ne a shekarar 1993.

Kungiyoyin kare hakki sun yi ta fafutukar ganin an soke dokar. Ɓangarori da dama na yaba wa ƙasar kan matakin soke hukuncin na kisa. In ji BBC.

Babbar jami’ar diflomasiyyar Birtaniya a Ghana Harriet Thompson, ta ce “Ghana ta shiga cikin dangin ƙasashen Commonwealth da suka dauki wannan mataki mai cike da tarihi.”

Birtaniya na adawa da hukuncin kisa a kowane hali kuma ta ce suna tare da Ghana a wannan batu.”

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp