fidelitybank

Ghana ta soke hukuncin kisa ga masu laifi

Date:

Majalisar dokokin Ghana ta soke hukuncin kisa, bayan da amince da yin gyara ga dokar hukumar manyan laifuka ta 2022. Ya biyo bayan tsawon lokaci na hanƙoro daga kungiyoyin kare hakkin bil adama na ganin an yi watsi da dokar.

Lauya mai hanƙoron kare hakkin dan’adam kuma dan majalisa Francis-Xavier Kojo Sosu ne ya miƙa wa majalisar kudirin dokar domin sauya ta tare da goyon bayan wata kungiya da ke Birtaniya mai rajin ganin an yi watsi da hukuncin kisa (Death Penalty Project).

Ya ce “A kan hukuncin kisa, fursunoni suna farkawa da tunanin cewa wannan ita ce ranarsu ta ƙarshe a duniya. Sun kasance kamar matattu masu rai, sun daina yi kamar mutane saboda haka soke hukuncin kisa zai nuna cewa a matsayinmu na al’umma mun kuɗuri aniyar cewa ba za mu kasance masu cin mutunci ko haifar da rashin zaman lafiya ba.”

A halin yanzu akwai maza 170 da mata 6 da aka yanke wa hukuncin kisa, waɗanda a yanzu za a maye gurbin hukuncin da daurin rai da rai.

Ko da yake kotuna a Ghana sun zartar da hukuncin kisan ne kan waɗanda aka samu da laifin kisan kai da yunkurin aikata kisa da kisan kare dangi da kuma fasa-ƙwaurin zinare; ba a cika aiwatar da hukuncin ba. Ghana ta zartar da hukuncin kisa na ƙarshe ne a shekarar 1993.

Kungiyoyin kare hakki sun yi ta fafutukar ganin an soke dokar. Ɓangarori da dama na yaba wa ƙasar kan matakin soke hukuncin na kisa. In ji BBC.

Babbar jami’ar diflomasiyyar Birtaniya a Ghana Harriet Thompson, ta ce “Ghana ta shiga cikin dangin ƙasashen Commonwealth da suka dauki wannan mataki mai cike da tarihi.”

Birtaniya na adawa da hukuncin kisa a kowane hali kuma ta ce suna tare da Ghana a wannan batu.”

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp