fidelitybank

Ghana ta koro ‘yan Najeriya da suka yi mata zamba

Date:

Reshen hukumar shige da fice na kan iyakar Seme a Najeriya ya ce Ghana ta tasa ƙeyar mutum 16 ‘yar Najeriyar zuwa gida saboda zargin su da aikata laifukan zamba ta intanet.

Kamfanin labarai na NAN ya ruwaito kwantirolan rundunar, Chukwu Emeka, yana faɗa a ranar Juma’a yayin taron manema labarai cewa matasa ne da suka fita daga Najeriyar don neman sana’o’in da za su riƙe kan su.

“Hukumomin Ghana na zargin su da aikata laifukan zamba, amma binciken farko-farko da muka gudanar ya nuna wasu daga cikinsu yaudararsu aka yi suka shiga harkokin sakamakon haɗamar da matasanmu ke da ita ta yin arziki cikin gaggawa,” a cewarsa.

Ya ci gaba da cewa: “An yaudari wasu daga cikinsu cewa za su yi arziki nan take idan suka bar Najeriya. Sai dai abin baƙin ciki shi ne ba su tarar da abin da aka yi musu alƙawari ba a Ghana.

Mista Emeka ya shawarci ‘yan Najeriya su dinga yin balaguro da takardun da suka dace ta yadda za su samu damar zama su yi sana’ar da suke so a ƙasashen da suka je ta hanyar bin doka da oda.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bankin Duniya zai kashe wa yankin Arewa a Najeriya dala miliyan 300

Bankin Duniya ya amince da kasafin kuɗi dala miliyan...

Giyar mulki na kwasar Trump – ‘Yan Majalisar Democrat

'Yan Democrats a Amurka sun zargi Donald Trump da...

Kama Aminu Waziri Tambuwal da EFCC ta yi ba daidai ba ne – PDP

Jam'iyyar PDP a jihar Sokoto ta yi Allah-wadai da...

An kai hari a ƙauyuka 15 na Zamfara a mako ɗaya – Rahoto

Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle...

Jihohin Arewa huɗu ne suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000 – NUP

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce...

A karon farko an gurfanar da Mutanen da ake zargi da kai hari Cocin Owo

Mutum biyar da ake zargi da shirya harin bam...

Peter Obi na nan a cikin jam’iyyar har yanzu – LP

Shugaban ƙungiyar Obidient Movement, Dr. Tanko Yunusa ya ce...

Yadda Mahara sun kashe mutum biyu, sun ƙona gidaje a Filato

Wasu da ake zargin mahara sun afka wa karamar...

An YI zanga-zanga a Isra’ila kan shirin Netanyahu na mamaye Gaza

Dubban mutane sun fito kan tituna a faɗin Isra'ila,...

Birtaniya za ta fara tisa ƙeyar bakin da suka aikata laifi zuwa kasarsu

Birtaniya ta fitar da sabon tsarin tisa keyar duk...

NDLEA ta kama Fasto kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Gwamnoni sun mika sakon ta’azziya ga iyalan Audu Ogbeh

Shugaban ƙungiyar gwamnonin arewa kuma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu...
X whatsapp