Kocin Black Galaxies ta Ghana, Mas-Ud Didi Dramani, ya fitar da tawagar ‘yan wasa 32 da zai buga da Najeriya wasan neman tikitin shiga gasar cin kofin Nahiyar Afrika (CHAN) na shekarar 2025.
A cewar wani bayani a shafin yanar gizon hukumar kwallon kafa ta Ghana (GFA), kungiyar za ta yi zango ne a Cibiyar Kwallon Kafa ta Ghanan da ke Prampram.
Kungiyar za ta yi matakai uku daban-daban na motsa jiki kafin wasan.
Ghana za ta karbi bakuncin wasan farko a ranar Asabar 21 ga watan Disamba, 2024, kuma za a buga wasan na biyu tsakanin 27-29 ga Disamba, 2024.
Wadanda suka yi nasara gaba daya za su tsallake zuwa CHAN 2025 wanda Kenya, Uganda da Tanzania za su dauki nauyin shiryawa.
Kungiyar Black Galaxies ta hana Najeriya samun tikitin shiga gasar a shekarar 2023.