Gwamnatin kasar Ghana ta janye dokar sanya takunkumi a fadin kasar.
Shugaban kasar, Nana Akufo-Addo, ya sanar da matakin a jiya Lahadi, yana mai bayar da misalin cewa, a yanzu an samu raguwa sosai na masu kamuwa da cutar korona.
Kazalika shugaban ya kuma cire bukatar gabatar da katin shaidar allurar rigakafin korona ga matafiyan da suka isa kasar a filin jirgin saman kasar da ke Accra.
Daga nan ya bukaci al’ummar kasar da su ci gaba da kula da tsabtar kansu da ma muhallansu da kuma kaucewa shiga taron jama’a.
Adadin masu kamuwa da cutar ya fara raguwa sosai tun daga karshen shekarar data wuce.
Ya zuwa yanzu an samu mutum kusan dubu dari da sittin da daya da suka taba kamuwa da korona a kasar.
Ghana dai ta shiga cikin jerin kasashen Afirka da suka sassauta dokokin korona duk da gargadin da Hukumar Lafiya ta Duniya ta yi cewa dage dokokin ya yi kusa.