fidelitybank

Gerrard ya tafi Turkiyya zuwa sabuwar ƙungiya

Date:

Tsohon dan wasan tsakiya na Ingila, Steven Gerrard ya tafi Istanbul don tattaunawa da Trabzonspor.

Gerrard bai da aiki tun bayan da Aston Villa ta kore shi a ranar 20 ga Oktoba.

Dan wasan mai shekaru 42 bai kai shekara daya a matsayin kocin kungiyar ta Premier ba, bayan da ya koma daga Rangers ya fara aiki a gasar firimiyar Ingila.

An danganta Gerrard da aikin Poland a farkon wannan shekarar, bayan da hukumar FA ta kasar ta yanke shawarar kin sabunta kwantiragin Czeslaw Michniewicz.

Amma daga baya Poland ta nada Fernando Santos.

A cewar kafar yada labaran Turkiyya Karar, Gerrard ya ziyarci Istanbul a farkon wannan mako domin cin abincin dare tare da Ertugrul Dogan, wanda ke neman zama shugaban Trabzonspor.

Kungiyar tana matsayi na shida a gasar Super Lig ta kasar Turkiyya, bayan da ta samu nasara a wasanni 11 cikin 23 da ta buga.

Rahotanni sun ce Dogan ya yi alkawarin daukar Gerrard a matsayin koci idan ya lashe zabe mai zuwa.

the punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp