Tsohon dan majalisar dokoki kuma mai sharhi kan al’umma, Sanata Shehu Sani, ya yi zargin cewa gazawar gwamnatin APC mai mulki na kara wa Bola Tinubu, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar bakin jini.
Bayanin nasa na kunshe ne a wani sako da ya wallafa a shafin sa na Twitter da aka tabbatar a ranar Alhamis.
Sani ya kuma yi ikirarin cewa Tinubu na fuskantar wani abu da ya bayyana a matsayin aiki mai sarkakiya, mai cin karo da juna da kuma rashin jin dadi na kare gazawar jam’iyyarsa ta APC yayin da a lokaci guda kuma ya yi alkawarin zai banbanta.
Ya rubuta cewa, “Mafi rikitarwa, sabani da rashin jin dadi na dan takarar shugaban kasa na jam’iyya mai mulki shi ne na kare gazawar jam’iyya mai mulki kuma a lokaci guda ya yi alkawarin zama daban.”