fidelitybank

Gawuna ne ya kamata ya maye gurbi na – Tsohon Minista

Date:

Tsohon ƙaramin ministan gidaje na Najeriya, Abdullahi Tijjani Gwarzo ya ce tsohon ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC, Nasiru Yusuf Gawuna ya kamata a bai wa muƙamin minista bayan sauke shi.

A wata hira da BBC ya ce tsohon ministan ya ce dalilin da aka bayar na sauke shi, shi ne wai yankin Kano ta arewa da ya fito, ‘yan siyasa masu muƙamai a tarayya sun yi yawa don haka ana son mayar da kujerarsa yankin Kano ta tsakiya.

”Kuma indai da gaske ake kano ta tsakiyar za a yi wa, ai ga ɗan takararmu nan na gwamnan – wanda shi ne jagoranmu a yankin Kano ta tsakiyar, me zai hana a ba shi”?

Ya ce muƙamin da ka bai wa Gawuna a yanzu, ba zai iya riƙe magoya bayansa da shi ba.

”Kuma duka sauran takwarorinsa da suka yi takara a wasu jihohin an ba su muƙamai, misali ga ɗan takarar jihar Plateau, da na Zamfara duk, an ba su minista”, in ji T Gwarzo.

Ya ƙara da cewa ya kamata a fara yi wa Gawuna tayin muƙamin, sai dai in shi ne ya ce ba ya so, to sai a bai wa wani.

”To amma shi ma wannan da aka bai wa ni bani da wani haufi da shi, tare muke komai a siyasa kuma ina yi masa fatan alkairi”.

legits news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp