Tsohon ƙaramin ministan gidaje na Najeriya, Abdullahi Tijjani Gwarzo ya ce tsohon ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC, Nasiru Yusuf Gawuna ya kamata a bai wa muƙamin minista bayan sauke shi.
A wata hira da BBC ya ce tsohon ministan ya ce dalilin da aka bayar na sauke shi, shi ne wai yankin Kano ta arewa da ya fito, ‘yan siyasa masu muƙamai a tarayya sun yi yawa don haka ana son mayar da kujerarsa yankin Kano ta tsakiya.
”Kuma indai da gaske ake kano ta tsakiyar za a yi wa, ai ga ɗan takararmu nan na gwamnan – wanda shi ne jagoranmu a yankin Kano ta tsakiyar, me zai hana a ba shi”?
Ya ce muƙamin da ka bai wa Gawuna a yanzu, ba zai iya riƙe magoya bayansa da shi ba.
”Kuma duka sauran takwarorinsa da suka yi takara a wasu jihohin an ba su muƙamai, misali ga ɗan takarar jihar Plateau, da na Zamfara duk, an ba su minista”, in ji T Gwarzo.
Ya ƙara da cewa ya kamata a fara yi wa Gawuna tayin muƙamin, sai dai in shi ne ya ce ba ya so, to sai a bai wa wani.
”To amma shi ma wannan da aka bai wa ni bani da wani haufi da shi, tare muke komai a siyasa kuma ina yi masa fatan alkairi”.