Tsohon shugaban hukumar yaki da masu yi wa arzikin kasa ta’annati EFCC Ibrahim Magu, ya ce, babu hujjar fitar shi daga hukumar EFCC.
Magu ya bayyana hakan ne a yayin wani bikin bayar da lambar yabo da kungiyar daliban matan arewa ta shirya domin girmama shi a ranar Lahadi a Abuja.
“Ni ina daga cikin mutanen da rashawa ta yaka, amma ina farin ciki kan abubuwan da suke faruwa a yanzu gaskiya na bayyana ga ‘yan Najeriya,” in ji shi.
Magu wanda dansa Mohammad-Saeed Ibrahim-Magu ya wakilta, ya yabawa kungiyar game da girmama shi da ta yi da wannan lambar yabo ta “cancanta” kuma yace yana cike da murnar karbar kyautar.
Da take nata bayanin kakakin kungiyar Aisha Nasir ta bayyana magu a matsayin wani mutum na daban, kuma jajurtacce, abin da ya sa ya cancanci kyautar kenan.
“Ko kana so ko baka so, Ibrahim Magu ya kai EFCC wani mataki a Najeriya wanda mutane da dama ba su taba zaton za ta iya kai wa ba.”