fidelitybank

Gasar Saudiyya ta fi ta Faransa kyau – Ronaldo

Date:

Shahararren ɗan wasa Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa gasar kwallon kafa ta Saudiyya ta zarta Ligue ta Faransa a halin yanzu.

Ya bayyana haka ne a ranar Juma’a a bikin karrama gwarazan ƴan wasa na Globe Soccer wanda aka yi a Dubai.

Ronaldo wanda ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasa na Gabas ta Tsakiya a bikin, ya ce yana da tabbacin gasar ta Saudiyya ta bunƙasa bayan shekara ɗaya da ya shafe a can, kuma ƙungiyoyi na fafatawa sosai.

“A gaskiya, ina ganin gasar Saudiyya ba ta fi ta Faransa muni ba. Muna da kyau fiye da gasar Faransa a yanzu,” in ji Ronaldo wanda ya lashe kyautar Ballon d’Or har sau biyar.

Ronaldo shi ne babban ɗan wasa na farko da ya fara komawa Saudiyya lokacin da ya kulla yarjejeniya da Al-Nassr a watan Janairun bara.

Ya ce yana da yakinin cewa nan gaba kaɗan gasar Saudiyya za ta zama ta uku a duniya, inda ya ce mutanen Saudiyya za su yi alfahari da hakan.

“Na fi kowa zura kwallaye a shekarar 2023, ina da shekara kusan 39… abin alfahari ne doke matasan ƴan kwallo irinsu Haaland,” in ji Ronaldo.

Gasar ta Saudiyya ta haɗa zaratan ƴan wasan kwallon kafa na duniya irin su Karim Benzema na Faransa, da Neymar na Brazil da kuma ɗan wasan Senegal Sadio Mane waɗanda duka suka bar Turai domin komawa ƙasar.

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp