fidelitybank

Ganga miliyan 107,239 na danyen mai ya yi batan dabo – Akanta

Date:

Ofishin babban mai binciken kudi na tarayya (AuGF) ya bayyana cewa a yanzu NNPC Limited, ya gaza yin lissafin kusan ganga 107,239,436.00 na danyen mai da aka dago don amfanin cikin gida a shekarar 2019.

Har ila yau AuGF ta ce, bayanan da aka samu daga rahoton ayyukan dakunan ajiya guda biyu sun nuna cewa, kimanin lita 22,929.84 na PMS da darajarsu ta kai Naira biliyan 7.06 da aka zuba a gidajen ajiyar guda biyu (Ibadan-Ilorin da Aba-Enugu) tsakanin watan Yuni da Yuli 2019 ba su samu ba.

Wannan fallasa ta kasance wani bangare ne na tambayoyi shida na tantancewa daga babban mai binciken kudi na tarayya, kamar yadda yake kunshe a cikin gwamnatin tarayyar Najeriya ta tattara bayanan kudi na shekarar da ta kare a ranar 31 ga watan Disamba, 2019 da aka mika wa magatakardar majalisar ta kasa ta wata wasika mai dauke da kwanan wata 18 ga watan Agusta, 2021, kuma babban mai binciken kudi, Adolphus Agughu ya sanya wa hannu.

Rahoton ya gano bambance da ke tsakanin adadin da NNPC ta bayar na mikawa asusun tarayya da kuma abin da AuGF ta ruwaito.

Ya ce yayin da bayanan NNPC ya nuna cewa N1,272,606,864,000.00 da kamfanin ya aika, adadin da Akanta Janar na tarayya ya rubuta ya kai N608,710,292,773.44, wanda ya nuna sabanin N663,896,567,227.

AuGF ta ce kamata ya yi a nemi Manajan Daraktan Rukunin na NNPC da ya yi bayanin sabanin da ke tsakanin wadannan alkaluman tare da tura ma’auni na N663,896,567,227.58 ga asusun tarayya ko kuma a hukunta shi.A cewar rahoton Tribune.

legits news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp