Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, zai bai wa mai martaba Sarkin Gaya, Alhaji Aliyu Ibrahim sandar girma a yau Asabar.
An dai nada mai martaba, Alhaji Aliyu Ibrahim ne a watan Satumban 2021 bayan rasuwar mahaifinsa Sarkin Gaya marigayi Ibrahim Abdulkadir.
Ko a kwanakin baya shekarar da ta gabata, gwamna Ganduje, ya baiwa mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero sandar girman, ta sa tun bayan da ya gaji kujerar Muhammadu Sunusi na II, bayan da gwamnan ya tsige shi daga kan karagar mulki.