Gwamna jihar Kano, Abdullahi Ganduje, ya ki amincewa da murabus din shugaban ma’aikatan sa, Ali Haruna Makoda da wasu kwamishinoni uku.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwar manema labarai mai dauke da sa hannun sakataren yada labaran gwamnan, Abba Anwar, wanda ya rabawa.
Ganduje, ya ki amincewa da murabus din Nura Muhammed Dankade, Sanusi Said Kiru, da Dr. Aminu Tsanyawa, kwamishinonin kasafin kudi da tsare-tsare, ilimi da lafiya.
Ya umarce su da su ci gaba da gudanar da ayyukansu.
Gwamnan, ya amince da murabus din wasu kwamishinonin sa guda bakwai, wato, Dr. Nasiru Yusuf Gawuna, Mataimakin gwamnan jihar Kano ya ajiye mukamin kwamishinan noma, Murtala Sule Garo, kwamishinan kananan hukumomi da al’adun gargajiya domin ya tsaya takara. dan takarar gwamnan jihar Kano a karkashin jam’iyyar APC, Ibrahim Ahmad Karaye – kwamishinan al’adu da yawon bude ido mai wakiltar mazabar Karaye/Rogo da Mahmoud Muhammad Santsi, kwamishinan sufuri na jihar Kano domin neman kujerar dan majalisar tarayya na jam’iyyar APC a kananan hukumomin Gabasawa da Gezawa.
Sauran sun hada da Musa Iliyasu Kwankwaso, Kwamishinan Raya Karkara mai wakiltar mazabar Kura/Madobi/ Garunmallam, Kabiru Ado Lakwaya, Kwamishinan Matasa da Wasanni na Jihar Kano don neman kujerar APC Gwarzo da Kabo a Karamar Hukumar Kabo a Jam’iyyar APC.
Gwamnan ya gode musu bisa gudunmawar da suke baiwa jihar tare da yi musu fatan alheri.