fidelitybank

Ganduje yaki amincewa da murabus din Kwamishinonin sa 3

Date:

Gwamna jihar Kano, Abdullahi Ganduje, ya ki amincewa da murabus din shugaban ma’aikatan sa, Ali Haruna Makoda da wasu kwamishinoni uku.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwar manema labarai mai dauke da sa hannun sakataren yada labaran gwamnan, Abba Anwar, wanda ya rabawa.

Ganduje, ya ki amincewa da murabus din Nura Muhammed Dankade, Sanusi Said Kiru, da Dr. Aminu Tsanyawa, kwamishinonin kasafin kudi da tsare-tsare, ilimi da lafiya.

Ya umarce su da su ci gaba da gudanar da ayyukansu.

Gwamnan, ya amince da murabus din wasu kwamishinonin sa guda bakwai, wato, Dr. Nasiru Yusuf Gawuna, Mataimakin gwamnan jihar Kano ya ajiye mukamin kwamishinan noma, Murtala Sule Garo, kwamishinan kananan hukumomi da al’adun gargajiya domin ya tsaya takara. dan takarar gwamnan jihar Kano a karkashin jam’iyyar APC, Ibrahim Ahmad Karaye – kwamishinan al’adu da yawon bude ido mai wakiltar mazabar Karaye/Rogo da Mahmoud Muhammad Santsi, kwamishinan sufuri na jihar Kano domin neman kujerar dan majalisar tarayya na jam’iyyar APC a kananan hukumomin Gabasawa da Gezawa.

Sauran sun hada da Musa Iliyasu Kwankwaso, Kwamishinan Raya Karkara mai wakiltar mazabar Kura/Madobi/ Garunmallam, Kabiru Ado Lakwaya, Kwamishinan Matasa da Wasanni na Jihar Kano don neman kujerar APC Gwarzo da Kabo a Karamar Hukumar Kabo a Jam’iyyar APC.

Gwamnan ya gode musu bisa gudunmawar da suke baiwa jihar tare da yi musu fatan alheri.

legit news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...
X whatsapp