fidelitybank

Ganduje ya yi wa Fursunoni 12 afuwa bayan an yanke musu hukuncin kisa

Date:

Gwamna Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya yi wa wasu fursunoni 12 da aka yanke wa hukuncin kisa afuwa.

A cikin wata sanarwa da mai magana da gidan ajiya da gyaran hali na jihar, SC Musbahu Lawan Nassarawa ya fitar, ta ce gwamnan ya yi wa ɗaurarrun afuwa ne duba da irin cunkoso da ake samu na waɗanda aka yanke wa hukuncin kisa.

Ya ce, tun da farko an yi niyyar yi wa fursunonin afuwa tun a bara, amma hakan bai yi wu ba, saboda sai da aka ɗauki lokaci aka tantance su.

Ya kuma ce, a yanzu an samu sauki na raguwar mutanen da aka yanke wa hukuncin kisa a gidajen yari, bayan afuwa da gwamnan ya yi wa wasu daga cikinsu.

Gwamnan ya kuma yafewa wasu fursunoni mata guda huɗu waɗanda suka shafe tsawon shekaru a ɗaure, saboda ganin kyakywan hali da suka nuna a lokacin da suke ɗaure.

An yi kira gare su da su zamo mutane masu kirki bayan komawa cikin al’umma da kuma cewa su guji duk abin da zai sake sa su koma gidan gyaran hali.

Sanarwar ta ce, wasu fursunonin da aka yi wa afuwa sun shafe shekaru 25 suna jiran aiwatar da hukuncin kisa a kansu.

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp