Gwamna jihar Kano, Dr. Abdullahi Ganduje, ya yi afuwa ga fursunoni kusan 90 a duk fadin gidan gyaran hali da ke jihar, domin murnar sallar Eid-el-Kabir.
Wata sanarwa da rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta fitar a ranar Asabar, ta ce, an yi wa fursunonin afuwa bisa laifuka daban-daban.
“An daidaita biya tarar fursunoni 77 tare da biyan diyya yayin da wasu fursunoni 10 da ke kan layin Mutuwa (IDR) suma gwamnan ya yi afuwa.”
Sanarwar ta ce, daga cikin fursunoni 10 da aka yanke musu hukuncin kisa, an yanke wa uku daga cikinsu hukuncin daurin rai-da-rai, ciki har da wata mace fursuna.
Hukumar gidan yarin ta ba da shaidar kyawawan halaye da sadaukar da fursunonin da aka ‘yanta, game da shirye-shiryensu na gyarawa tare da nuna nadama kan laifukan da suka aikata.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa, baya ga ’yancin, Ganduje ya ba su Naira 5,000 kowannensu, domin su yi kudin jigila zuwa gidajensu.