Gwamnan jihar Kano, Dr Abdullahi Ganduje, ya amince da nadin Malam Usman Muhammad a matsayin shugaban ma’aikata na jihar.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran sa Abba Anwar ya fitar jiya.
Anwar ya ce, gwamnan ya kuma amince da nadin sabbin sakatarorin dindindin guda hudu a ma’aikatan gwamnatin jihar.
Ya ce, Muhammad ya kasance babban sakatare a ma’aikatar yada labarai kafin nadin nasa.
Sabbin Sakatarorin Dindindin sun hada da Muhammad Shehu, wanda har zuwa lokacin da aka nada shi, shi ne Daraktan Bincike da Kididdiga na Hukumar Kula da Hanyoyi ta Jihar (KARMA).
Sauran su ne,vMalam Magaji Lawan wanda shi ne Daraktan kudi da asusu na ma’aikatar kudi kafin nadin sa.
“Saura biyun su ne, Bilyaminu Zubairu, da Malama Mairo Dambatta,” in ji Anwar.
Yace nade-naden ya fara aiki ne nan take.