Ministan Koyar da sana’o’i na Jamhuriyar Nijar, Kassoum Mamane Moctar, ya ce, kasarsa ta Nijar ta gamsu da irin tsare-tsare da ayyukan da gwamnatin Dr. Abdullahi Umar Ganduje ke yi, domin ci gaban matasa.
Moctar ya yi wannan jawabin ne a ranar Talata, yayin da ya kai wa Gwamna Ganduje ziyara a gidan gwamnatin Kano.
Sanarwar da babban sakataren yada labarai na mataimakin gwamnan Kano, Hassan Musa Fagge, ya fitar ta ce, Ministan ya kara da cewa tsare-tsaren na cigaban matasa da gwamnatin Kano ta fitar abin koyi ne.
Ministan ya ce, nasarorin da gwamnatin Kano ta samu a bangaren matasan, yasanya Nijar ta tura tawaga zuwa Kano, domin yin nazari kan tsare-tsaren koyar da matasa sana’o’in dogaro da kai.
A nasa jawabin Gwamna Ganduje ya ce, gwamnatinsa ta gano cewa, cigaban matasa ne ginshikin ci gaba da kawar da ayyukan laifi, shi yasa ta mayar da hankali a bangaren.