fidelitybank

Ganduje ya rattaba hannu a kan dokar inganta rayuwar nakasassu

Date:

Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya sanya hannu a kan dokar inganta rayuwar masu bukata ta musamman, wadda majalisar dokokin jihar ta zartar kwanan nan.

Gwamnan ya ce dokar za ta taimaka wajen sanya masu larurar nakasa a cikin tsare-tsaren gwamnati da suka shafi cigaban kasa.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano ya ce wanzuwar wannan doka ta inganta rayuwar masu larurar nakasa za ta ba da damar fito da wannan bangare na al`umma da nau’o’in bukatunsu ta yadda za a shigar da su a cikin tsarin gwamnati, tare da share musu hawaye.

Dokar ta hana yi musu kallon kaskanci, sannan ta yi tsari na saukaka musu rayuwa wajen shige da fice a gine-gine da ma’aikatun gwamnati – ga kuma tanadin da ya ti na kaso na musamman na guraben aiki domin masu larurar nakasar.

Malam Yerima Sulaiman Ibrahim na cikin shugabannin masu bukata ta musamman din a Najeriya, kuma daya daga cikin jagororinsu a jihar Kano, wanda ya ce suna murmushi har kunne, sakamakon sanya hannu da gwamnan ya yi a kan wannan doka.

Sai dai ganin cewa gwamnan ya rattaba hannu a kan wannan dokar ne a wata gaba da wa’adin mulkinsa ke karewa.

Wannan ne ya sa Malam Yerima Sulaiman ya ce, mutanensa na so gwamnan ya yi wani abu kasa da zai sa hukumar kula da masu larurar nakasar ta dore har bayan zamaninsa:

A makon jiya ne majalisar dokokin jihar Kano ta zartar da wannan doka ta inganta rayuwar masu bukata ta musamman din.

Sai ga shi a wannan makon gwamna Ganduje bai tsaya wata-wata ba–ya rattaba mata hannu.

Wadanda aka yi dokar domin su sun hada da masu larurar rashin gani, rashin kafa ko hannu, da larurar ji, da ta fata ko zabiya da larurar rashin yatsa wato kuturta da masu cutar laka da kuma galahanga.

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Za mu ladabtar da Jami’an mu da aka gansu suna taimakawa ‘yan siyasa a Kano – ‘Yansanda

Rundunar Æ´an sanda ta jihar Kano ta ce, ta...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baÉ—ala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...

NNPP ta yi tafka magudi a zabencike gurbin Kano – Farouk Lawan

Tsohon dan majalisar wakilai, Farouk Lawan, ya yi zargin...

Dan shugaban kungiyar Boko Haram ya shiga hannu

Hukumomi a ƙasar Chadi sun kama yaron shugaban ƙungiyar...

Daga yau wankin koda a Najeriya ya koma dubu 12 maimakon dubu 50 – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya amince da rage farashin...

An ceto Mutane 25 da syka kife a kwale-kwalen Sokoto

Hukumomi a jihar Sokoto sun ce, sun samu nasarar...

An fara duba rabon gyaran arzikin Najeriya

Shugaban Hukumar rarraba arziƙin ƙasa RMAFC, Mohammed Shehu, ya...
X whatsapp