Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano, ya nada Zahara’u Nasir Ahmed a matsayin babbar mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai, nan take.
Nadin na ta a cewar gwamnan, ya biyo bayan nazari sosai kan irin dimbin gogewar da ta samu a aikin yada labarai, tare da la’akari da kokarinta na ganin ta samu kwarewa ta kowane fanni,” in ji shi.
Sanarwar da Abba Anwar babban sakataren yada labarai na Gwamnan Jihar Kano ya sanyawa hannu tare da raba wa manema labari, ya ce, gwamnan ya yi mata addu’ar samun nasara, tare da umartar ta da ta yi aiki tukuru tare da sauran mataimakan kafafen yada labarai tare da tsayawa kan kwarewa tare da yarda da tsarin aikin.