Gwamna Abdullahi Ganduje na jihar Kano, ya kaddamar da zababbun shugabannin jam’iyyar a fadin kananan hukumomin jihar 44 a mazabu 484, gabanin babban taron jam’iyyar APC na kasa.
Taron nadin wanda ya gudana bisa ga shiyya-shiyya, an kammala shi da Sanatan Kano ta Arewa a ranar Talata.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakataren yada labaran gwamnan, Abba Anwar, kuma aka rabawa manema labarai a Kano ranar Laraba.
A kowane shagulgulan, Ganduje ya dage cewa, “A matsayina na zababbun jami’an jam’iyyar, wanda tsarin zaben jam’iyyar da aka saba ya tabbatar da zabensu da kotun daukaka kara ta sake tabbatar da shi, ya kamata ku jajirce wajen ganin jam’iyyarmu ta kara karfi.
“Kano kasancewar ita ce babbar dimokuradiyya a Najeriya, muna da dalilai masu yawa na tsara hanyoyin dorewar dimokuradiyya da karfafa dimokuradiyya a kasar nan. Ya kamata ku je duk lungu da sako na jihar ku tabbatar da cewa jam’iyyarmu ta ci gaba da yin karfi,” in ji Anwar Gwamnan a cikin sanarwar.
Jimillar kananan hukumomi 16 da suka kunshi mazabu 172 daga Kano ta Kudu suna da jami’an jam’iyyar 4,644 daga mazabu 172 da kuma jami’ai 432 daga kananan hukumomin 16.
Yayin da Kano ta tsakiya mai kananan hukumomi 15 ta na da mazabui 172. Akwai jami’an jam’iyyar 4,644 daga mazabu 172 da kuma jami’ai 405 daga kananan hukumomin 15.