Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya naɗa Alaramma Ahmed Sulaiman a matasayin kwamishina na biyu a hukumar kula da makarantun firamare ta jihar Kano.
Alaramma Ahmad Sulaiman ne ya tabbatar da ba shi wannan muƙamin a saƙon da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya yi godiya ga gwamnan.
BBC ta rawaito cewa Alarama ya wallafa hotunansa tare da gwamnan, a gefe akwai Sheikh Abdullahi Balalau wanda shi ne shugaban Ƙungiyar Izala, da kuma sakataren ƙungiyar na ƙasa Sheikh Kabir Gombe.