fidelitybank

Ganduje ya naɗa kwamitin da zai yi sulhu a kan rikicin gwamnan Ondo

Date:

A ranar Alhamis din da ta gabata ne shugaban jam’iyyar APC na kasa, Alhaji Abdullahi Ganduje, ya kafa kwamitin mutane tara domin shiga tsakani a rikicin tsige gwamnatin jihar Ondo.

Mista Edwin Olofu, babban sakataren yada labarai na Ganduje ne ya bayyana hakan a wata sanarwa.

Ya ce kwamitin karkashin jagorancin Aminu Masari, tsohon gwamnan jihar Katsina, zai kuma nemi a sasanta duk bangarorin da abin ya shafa.

“Gaskiya babbar sakatariyar jam’iyyar ta kasa ta damu da irin halin da ake ciki a siyasance a jihar Ondo, wanda idan ba a gaggauta kawar da shi ba, zai iya haifar da rashin jituwa a tsakanin mabiya jam’iyyar.

“Saboda haka, domin a kawar da rashin fahimtar juna, kuma bayan lura da lamarin, sakatariyar kasa ta yanke shawarar kutsa kai.

“Da nufin samar da ingantacciyar fahimtar da za ta iya kaiwa ga cimma matsaya ta gaskiya,” in ji Ganduje.

Ya kuma tabbatar wa ‘ya’yan jam’iyyar cewa kwamitin zai yi mu’amala tare da tattaunawa da dukkan masu ruwa da tsaki a jihar bisa mutunta juna, da nufin samar da mafita mai dorewa a kan rikicin.

Ya kuma bukaci dukkanin bangarorin da su kwantar da hankulansu tare da baiwa kwamitin da Masari ya jagoranta hadin kai da goyon baya.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp