fidelitybank

Ganduje ya naɗa kwamitin da zai yi sulhu a kan rikicin gwamnan Ondo

Date:

A ranar Alhamis din da ta gabata ne shugaban jam’iyyar APC na kasa, Alhaji Abdullahi Ganduje, ya kafa kwamitin mutane tara domin shiga tsakani a rikicin tsige gwamnatin jihar Ondo.

Mista Edwin Olofu, babban sakataren yada labarai na Ganduje ne ya bayyana hakan a wata sanarwa.

Ya ce kwamitin karkashin jagorancin Aminu Masari, tsohon gwamnan jihar Katsina, zai kuma nemi a sasanta duk bangarorin da abin ya shafa.

“Gaskiya babbar sakatariyar jam’iyyar ta kasa ta damu da irin halin da ake ciki a siyasance a jihar Ondo, wanda idan ba a gaggauta kawar da shi ba, zai iya haifar da rashin jituwa a tsakanin mabiya jam’iyyar.

“Saboda haka, domin a kawar da rashin fahimtar juna, kuma bayan lura da lamarin, sakatariyar kasa ta yanke shawarar kutsa kai.

“Da nufin samar da ingantacciyar fahimtar da za ta iya kaiwa ga cimma matsaya ta gaskiya,” in ji Ganduje.

Ya kuma tabbatar wa ‘ya’yan jam’iyyar cewa kwamitin zai yi mu’amala tare da tattaunawa da dukkan masu ruwa da tsaki a jihar bisa mutunta juna, da nufin samar da mafita mai dorewa a kan rikicin.

Ya kuma bukaci dukkanin bangarorin da su kwantar da hankulansu tare da baiwa kwamitin da Masari ya jagoranta hadin kai da goyon baya.

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp