Gwamna Abdullahi Ganduje na jihar Kano, ya kaddamar da aikin samar da tituna a garin Garo da makwaftan karamar hukumar Kabo da ke jihar.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakataren yada labaran gwamnan, Abba Anwar, kuma aka rabawa manema labarai a Kano ranar Lahadi.
Gwamna Ganduje ya samu wakilcin kwamishinan kananan hukumomi da masarautu Murtala Sule Garo, tare da goyon bayan kwamishinan ayyuka da raya ababen more rayuwa Injiniya. Idris Wada, a wajen bikin kaddamar da aikin a ranar Asabar.
Garo ya bada tabbacin gwamnatin Ganduje za ta yi aiki ba dare ba rana, domin inganta ayyukan more rayuwa a yankunan karkara.
“Akwai hanya mai nisan kilomita 18 daga Kanye-Kabo-Dugabau, wacce ta ratsa unguwanni takwas daga cikin Unguwani goma na karamar hukumar Kabo. An fara aikin ne a cikin 2018 kuma an watsar da aikin rabin hanyar. In ji shi.