Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, a ranar Lahadin ya jajantawa iyalan malaman addinin Islama guda shida da suka rasa rayukansu a wani hatsarin mota da ya rutsa da su yayin da suke dawowa daga karamar hukumar Sumaila kwanan nan.
“Mutuwar wadannan mutanen ba babban rashi ne ga iyalansu kadai ba, har ma ga jihar baki daya. Abin takaici ne,” inji shi.
“Mun samu labarin cewa Malaman da Sheikh Alkassim Zakariyya ya jagoranta sun fara ziyarar aiki karkashin inuwar Imam Malik Islamic Foundation.
A wata sanarwa da babban sakataren yada labaran Abba Anwar ya rabawa manema labarai, ya ruwaito Gwamna Ganduje yana cewa: “Jahar mu ta yi asarar mutane masu tsoron Allah, daga cikinsu akwai Sheikh Alkassim, Malam Isiya Tela, Mustapha Musa Sa’ad, Malam Ishaq. Rummawa da Malam Zakariyya Alkassim Dataka. Allah Ya gafarta musu,” inji shi.