Gabanin zaben 2023, gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya bayar da wa’adin sa’o’i 24 ga duk wani dan siyasa da ke neman tsayawa takara ya yi murabus daga gwamnatin sa.
A cikin wata sanarwa mai sakin layi uku mai dauke da sa hannun babban sakataren yada labaran sa, Abba Anwar ya fitar, ta ce, Ganduje ya ba da umarnin cewa, wadanda aka nada su ajiye aikin su daga ranar Litinin ko kuma kafin ranar Litinin 18 ga Afrilu, 2022.
A cewarsa, “duk masu rike da mukaman siyasa da ke neman mukaman siyasa a zaben 2023 mai zuwa su yi murabus daga mukamansu.
“An ba su daga yanzu zuwa Litinin 18 ga Afrilu, 2022, su yi murabus. Umurnin yana bin sashe na 84 (12) na sabuwar dokar zabe da aka yi wa kwaskwarima,” in ji Anwar a cikin sanarwar.