Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya naɗa Aliko Dangote, Aminu Dantata da Abdussamad Isyaku Rabiu a matsayin mambobi na kwamitin gudanarwa na Hukumar Zakka da Hubusi ta Kano.
Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Muhammad Garba ne ya baiyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a yau Laraba, inda ya ce naɗin ya samu ne bayan taron Majilisar Zartsawa na Mako-mako.
Ya ce Dr Ibrahim Muazzam Maibushira, shi ne a ka naɗa a matsayin Shugaban kwamitin.
Sauran, a cewar Kwamishinan, sun haɗa da Dr AbdulMutallab Ahmed a matsayin Kwamishina I sai kuma Dr Lawi Sheikh Atiq a matsayin Kwamishina na ll a hukumar.
Sauran sun haɗa da wakilan Masarautar Kano, wakilan Ma’aikatar Yaɗa Labarai, Wakilan Ma’aikatar Harkokin Addinai, sai kuma wakilan kasuwannin kurmi, Rimi, Kwari da Singa.
Hakazalika Garba ya sanar da cewa Majalisar Zartaswar ta sahale da kafa kwamitin da zai tantance Cibiyar Addinin Musulunci ta Duniya.
Ya ƙara da cewa Babban Limamin Kano, Farfesa Sani Zaharaddeen ne zai shugabanci kwamitin, inda Dakta Muhammad Tahar Adam, Kwamishinan Harkokin Addinai zai zama Shugaban na 2, sai Auwalu Yakasai a matsayin sakatare.