fidelitybank

Ganduje na kokarin sasanta Uzodinma da Rochas

Date:

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa Dakta Abdullahi Umar Ganduje da mataimakin shugaban Najeriya sanata Kashim Shettima na yunƙurin sasanta tsakanin gwamnan jihar Imo Hope Uzodinma da tsohon gwamnan jihar Sanata Rochas Okorocha gabanin zaɓen gwamnan jihar da ke tafe.

Cikin wani saƙon ‘X’ da a baya aka fi sani da Tuwita, da APC ta wallafa ta ce ‘gabanin zaɓen gwamna da ke tafe a jihar Imo, APC gida ne na haɗin kai don ƙarfafa juna”.

Jam’iyyar ta kuma wallafa hotunan mutanen biyu na gaisawa da juna, ga kuma shugaban jam’iyyar da mataimakin shugaban ƙasar.

Mutanen biyu waɗanda su ne jiga-jigan jam’iyyar APC a jihar sun samu saɓani tsakaninsu, inda suka ƙwashe lokaci suna takun-saƙa.

A shekarar 2021 ne Uzodinma ya samu umarnin kotu wajen ƙwace wani kadarar Okorocha da ke jihar.

A lokacin Okorocha ya yi yuƙurin ɗaukaka ƙara, amma jami’an tsaro suka kama shi, kodayake an sake shi a ranar.

Saɓani tsakanin mutanen biyu ta faro ne tun a zaɓen 2019 a lokacin da Okorocha ya zaɓi bai wa surukinsa takarar gwamnan jihar, maimakon Uzodinma.

Lamarin da ya haifar da ‘yan takarar gwamna biyu a ƙarƙashin APC, sai dai daga baya uwar jam’iyyar ta ƙasa – ƙarƙashin Adam Oshimole – ta ce Uzodinma ne halastacen dan takara.

Tun bayan da ya zama shugaban jam’iyyar na ƙasa Abdullahi Ganduje ya alƙawarta tabbatar da haɗin kan jam’iyyar, domin samun nasara a zaɓuka masu zuwa musamman na jihohin Imo da Kogi da kuma Bayelsa.

A ranar 11 ga watan Nuwamba ne za a gudanar da zaɓen gwamna a jihar Imo.

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp