Kungiyar masu gudanar da harkokin tallace-tallace kafofin yada labarai ta kasa (MIPAN) ta karrama Gwamna jihar Kano, Dr.Abdullahi Umar Ganduje.
Kungiyar ta baiwa gwamnan lambar yabo ne a matsayin “Uban Kungiyar” saboda irin gudunmawar da ya bayar ga cigaban kafofin yada labarai da ayyukan raya kasa da kuma tallafawa al’umma.
Mataimakin Gwamna jihar Kano, Dr. Nasiru Yusuf Gawuna shi ne ya wakilci gwamna Ganduje, a taron da ya gudana a ranar Alhamis a otal din Radisson Blu din da ke unguwar Ikeja a jihar Lagos.