fidelitybank

Ganduje da Kwankwaso su haɗe kan su don a ciyar da Kano gaba – Murtala Sule Garo

Date:

Domin a warware takaddamar siyasar Kano, kuma a samu hadin kai, dole ne mai girma tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje da magabatansa, Rabiu Kwankwaso da Ibrahim Shekarau, su kawar da sabanin da ke tsakaninsu, su hada kai domin ci gaban jihar.

Wannan shine matsayin tsohon kwamishinan al’amuran kananan hukumomi na jihar Kano kuma dan takarar mataimakin gwamnan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a 2023, Murtala Sule Garo.

Ya bayyana damuwarsa kan rashin jituwar da ta kunno kai tsakanin tsaffin gwamnonin jihar yayin da yake jawabi a wajen taron tsaffin ‘yan majalisar dokokin jihar Kano na 8 da 9.

Garo ya yi kira ga Ganduje da Kwankwaso da su ajiye sabanin da ke tsakaninsu su hada kai domin ci gaban jihar Kano.

“Roƙona shi ne ga tsoffin gwamnoninmu. Abin takaici ne ganin yadda a Jiha irin ta Zamfara da ke bayan Kano ta fuskoki da dama, tsofaffin Gwamnonin nasu suna taruwa suna taro duk da bambancin siyasa da akidunsu. Suna ganawa da tattauna batutuwan da suka shafi ci gaban jiharsu.

“Amma a nan Kano, abin mamaki da ban takaici ne yadda shugabanninmu da dattawanmu, tsofaffin gwamnoni, ba za su iya haduwa don tattaunawa kan al’amuran da za su kawo ci gaban Kano ba.

“Saboda haka, muna rokonsu, kuma muna musu addu’a da su sasanta su kuma ajiye bambance-bambancen da ke tsakaninsu idan da gaske suna son ci gaban jihar Kano,” in ji Garo.

Rikicin Ganduje da abokin siyasa kuma amininsa Kwankwaso ya faru ne nan da nan bayan zaben gwamna na 2015, wanda ya sa Ganduje ya samu nasara kuma ya zama magajin Kwankwaso.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp