Domin a warware takaddamar siyasar Kano, kuma a samu hadin kai, dole ne mai girma tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje da magabatansa, Rabiu Kwankwaso da Ibrahim Shekarau, su kawar da sabanin da ke tsakaninsu, su hada kai domin ci gaban jihar.
Wannan shine matsayin tsohon kwamishinan al’amuran kananan hukumomi na jihar Kano kuma dan takarar mataimakin gwamnan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a 2023, Murtala Sule Garo.
Ya bayyana damuwarsa kan rashin jituwar da ta kunno kai tsakanin tsaffin gwamnonin jihar yayin da yake jawabi a wajen taron tsaffin ‘yan majalisar dokokin jihar Kano na 8 da 9.
Garo ya yi kira ga Ganduje da Kwankwaso da su ajiye sabanin da ke tsakaninsu su hada kai domin ci gaban jihar Kano.
“Roƙona shi ne ga tsoffin gwamnoninmu. Abin takaici ne ganin yadda a Jiha irin ta Zamfara da ke bayan Kano ta fuskoki da dama, tsofaffin Gwamnonin nasu suna taruwa suna taro duk da bambancin siyasa da akidunsu. Suna ganawa da tattauna batutuwan da suka shafi ci gaban jiharsu.
“Amma a nan Kano, abin mamaki da ban takaici ne yadda shugabanninmu da dattawanmu, tsofaffin gwamnoni, ba za su iya haduwa don tattaunawa kan al’amuran da za su kawo ci gaban Kano ba.
“Saboda haka, muna rokonsu, kuma muna musu addu’a da su sasanta su kuma ajiye bambance-bambancen da ke tsakaninsu idan da gaske suna son ci gaban jihar Kano,” in ji Garo.
Rikicin Ganduje da abokin siyasa kuma amininsa Kwankwaso ya faru ne nan da nan bayan zaben gwamna na 2015, wanda ya sa Ganduje ya samu nasara kuma ya zama magajin Kwankwaso.