fidelitybank

Ganawar gwamnatin Najeriya da ta Nijar ko akwai alfanu?

Date:

Ministocin harkokin wajen Najeriya da Nijar sun gudanar da wata tattaunawa ta musamman kan al’amura da dama da suka shafi harkokin tsaro da tattalin arziki a kan iyakokin ƙasashen biyu.

Hakan dai na zuwa ne bayan da Najeriya ta sake sabunta kiraye-kirayen neman a saki hamɓararren shugaban Jamhuriyar Nijar Mohamed Bazoum, wanda ke tsare a fadar shugaban ƙasar da ke Yamai.

Ministan harkokin wajen Najeriya Yusuf Tuggar ya tattauna da ministan harkokin wajen Nijar Bakary Yaou Sangare, a ziyara ta biyu da wani babban jami’in Najeriya ya kai tun bayan juyin mulkin da aka yi a ƙasar a 2023, bayan Janar Christopher Musa, babban hafsan tsaron Najeriya ya ziyarci Nijar a watan Agustan bara,

”Tattaunawar ta gudana ne cikin yanayi mai cike da mutuntawa ta kuma bayar da damar yin nazari mai zurfi kan ƙalubalen da ƙasashen biyu ke fuskanta,” in ji wata sanarwar haɗin gwiwa da ministocin biyu suka fitar.

A ɓangaren tattalin arziki, ministocin sun tattauna kan aikin layin dogo da zai haɗa garuruwan Kano da Katsina na Najeriya zuwa Maradi a Nijar, wanda za a buɗe a shekarar 2026.

Har ila yau, sun tattauna batun gina babbar hanyar Trans-Sahara, da shirin bututun iskar gas da za a yi a yankin Sahara, da kuma batutuwan da suka shafi haraji.

Nijar da Burkina Faso da Mali sun fice daga ƙungiyar tattalin arzikin ƙasashen yammacin Afirka a farkon wannan shekara, inda suka zargi ƙungiyar ECOWAS da gazawa wajen yaƙi da masu iƙirarin jihadi.

Dukkanin ƙasashen uku dai na ƙarƙashin jagorancin sojoji ne, kuma suna fuskantar munanan hare-hare daga ƙungiyoyi masu iƙirarin jihadi.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...
X whatsapp