Ministocin harkokin wajen Najeriya da Nijar sun gudanar da wata tattaunawa ta musamman kan al’amura da dama da suka shafi harkokin tsaro da tattalin arziki a kan iyakokin ƙasashen biyu.
Hakan dai na zuwa ne bayan da Najeriya ta sake sabunta kiraye-kirayen neman a saki hamɓararren shugaban Jamhuriyar Nijar Mohamed Bazoum, wanda ke tsare a fadar shugaban ƙasar da ke Yamai.
Ministan harkokin wajen Najeriya Yusuf Tuggar ya tattauna da ministan harkokin wajen Nijar Bakary Yaou Sangare, a ziyara ta biyu da wani babban jami’in Najeriya ya kai tun bayan juyin mulkin da aka yi a ƙasar a 2023, bayan Janar Christopher Musa, babban hafsan tsaron Najeriya ya ziyarci Nijar a watan Agustan bara,
”Tattaunawar ta gudana ne cikin yanayi mai cike da mutuntawa ta kuma bayar da damar yin nazari mai zurfi kan ƙalubalen da ƙasashen biyu ke fuskanta,” in ji wata sanarwar haɗin gwiwa da ministocin biyu suka fitar.
A ɓangaren tattalin arziki, ministocin sun tattauna kan aikin layin dogo da zai haɗa garuruwan Kano da Katsina na Najeriya zuwa Maradi a Nijar, wanda za a buɗe a shekarar 2026.
Har ila yau, sun tattauna batun gina babbar hanyar Trans-Sahara, da shirin bututun iskar gas da za a yi a yankin Sahara, da kuma batutuwan da suka shafi haraji.
Nijar da Burkina Faso da Mali sun fice daga ƙungiyar tattalin arzikin ƙasashen yammacin Afirka a farkon wannan shekara, inda suka zargi ƙungiyar ECOWAS da gazawa wajen yaƙi da masu iƙirarin jihadi.
Dukkanin ƙasashen uku dai na ƙarƙashin jagorancin sojoji ne, kuma suna fuskantar munanan hare-hare daga ƙungiyoyi masu iƙirarin jihadi.