Shugaban Riƙon Ƙwarya na Gabon, Brice Oligui Nguema ya dakatar da jami’an gwamnatinsa na riqon ƙwarya tafiya hutu a ƙasashen waje, a wani yunƙuri da ya dace da tsarin shugabacinsa.
An bayar da sanarwar ce a wata wasiƙa da aka karanta a talabijin ɗin ƙasar, inda jagororin juyin mulkin suka sanar da cewa hutun mako ɗaya ne kawai jami’in gwamnati yake da shi a shekara.
“Dole a cikin kasar nan kowa zai yi hutunsa, sannan duk wanda zai yi hutu, asalin garinsa zai koma domin su riƙa shiga cikin harkokin mutanensu na yau da kullum,” kamar yadda sanarwar ta nuna.
Wannan na zuwa ne bayan Janar Nguema ya zagaya cikin ƙasar, inda ya tattauna da mutanen ƙasar, sannan ya saurari matsalolinsu.
“Wannan matakin zai taimaka wajen ƙarfafa gwiwar komawa gida, sannan zai ƙara kawo kusanci da mutane,” inji kakakin gwamnatin sojin, sannan ya ƙara da cewa za a iya samun akasin hakan ne kawai domin rashin lafiya ko kuma wani lamarin da zai iya zuwa ba zato ba tsammani.
Tun bayan da Janar Oligui ya yi juyin mulki daga tsohon Shugaban Ƙasar Ali Bongo a bara, ya dage wajen nuna wa mutanen ƙasar cewa gwamnatinsa ta mutane ce. Wannan matakin ne hana jami’an gwamnati tafiya hutu a ƙasashen waje na zuwa makonni ƙaɗan bayan shekara ɗaya da juyin mulkin da aka hamɓarar da Ali Bongo.
Haka kuma wadannan matakan suna zuwa ne a daidai lokacin da ake raɗe-raɗin cewa Janar Nguema yana kamun ƙafa ne domin tsayawa takarar Shugaban Ƙasa, wanda ake sa ran za a yi a Agustan baɗi.
Sai dai har yanzu bai fito fili ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar ba.