fidelitybank

Gabon ta haramta wa jami’an gwamnati zuwa hutu kasashen waje

Date:

Shugaban Riƙon Ƙwarya na Gabon, Brice Oligui Nguema ya dakatar da jami’an gwamnatinsa na riqon ƙwarya tafiya hutu a ƙasashen waje, a wani yunƙuri da ya dace da tsarin shugabacinsa.

An bayar da sanarwar ce a wata wasiƙa da aka karanta a talabijin ɗin ƙasar, inda jagororin juyin mulkin suka sanar da cewa hutun mako ɗaya ne kawai jami’in gwamnati yake da shi a shekara.

“Dole a cikin kasar nan kowa zai yi hutunsa, sannan duk wanda zai yi hutu, asalin garinsa zai koma domin su riƙa shiga cikin harkokin mutanensu na yau da kullum,” kamar yadda sanarwar ta nuna.

Wannan na zuwa ne bayan Janar Nguema ya zagaya cikin ƙasar, inda ya tattauna da mutanen ƙasar, sannan ya saurari matsalolinsu.

“Wannan matakin zai taimaka wajen ƙarfafa gwiwar komawa gida, sannan zai ƙara kawo kusanci da mutane,” inji kakakin gwamnatin sojin, sannan ya ƙara da cewa za a iya samun akasin hakan ne kawai domin rashin lafiya ko kuma wani lamarin da zai iya zuwa ba zato ba tsammani.

Tun bayan da Janar Oligui ya yi juyin mulki daga tsohon Shugaban Ƙasar Ali Bongo a bara, ya dage wajen nuna wa mutanen ƙasar cewa gwamnatinsa ta mutane ce. Wannan matakin ne hana jami’an gwamnati tafiya hutu a ƙasashen waje na zuwa makonni ƙaɗan bayan shekara ɗaya da juyin mulkin da aka hamɓarar da Ali Bongo.

Haka kuma wadannan matakan suna zuwa ne a daidai lokacin da ake raɗe-raɗin cewa Janar Nguema yana kamun ƙafa ne domin tsayawa takarar Shugaban Ƙasa, wanda ake sa ran za a yi a Agustan baɗi.

Sai dai har yanzu bai fito fili ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar ba.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...
X whatsapp