Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, ya bayar da tabbacin cewa, jam’iyyar PDP, za ta tarbi masu sauya sheka daga sauran jam’iyyun siyasa gabannin zaben 2023.
Tambuwal ya bayyana hakan ne a ranar Talata, 8 ga watan Fabrairu, yayin ziyararsa ta uku kan neman shawara game da kudirinsa na neman tikitin shugaban kasa na PDP, a birnin Kebbi, jihar Kebbi.
Tambuwal wanda ya samu rakiyar tsohon gwamnan jihar Sokoto, Attahiru Bafarawa da tsohon mataimakin gwamnan Sokoto Mukhtar Shagari da tsohon ministan lantarki, Injiniya Bello Suleiman, ya yaba da hadin kan da jiga-jigan PDP a Kebbi da mabiyansu suka nuna a zaben karamar hukuma da aka yi kwanan nan.
Tambuwal ya kuma koka kan yadda Najeriya ke shirin rugujewa, sakamakon rashin tsaro da tsarin kiwon lafiya mara inganci, talauci, tabarbarewar ilimi, cin hanci da rashawa da sauran yanayi da gwamnatin APC ta jefa kasar a ciki.
Bafarawa wanda ya bayyana ziyarar a matsayin na gida, ya nuna farin ciki da karamcin da PDP reshen jihar Kebbi ta nuna a yayin zaben kananan hukumomi a jihar.