Tsohon kwamishinan ayyukan jihar Kano, Mu’az Magaji, ya ce, tsagin G7 zai tarbi wasu manyan ‘yan adawa daga tsagin Kwankwasiyya.
Mu’az Magaji ya ce, akwai wasu jiga-jigan tafiyar Kwankwasiyya da za su tsallako bangarensu na G7.
Daga cikin wadanda ya ce, za su dawo APC akwai Yunusa Dangwani da Madakin Gini da Danburam.
Tsohon kwamishinan ayyuka na jihar Kano, Mu’az Magaji wanda aka fi sani da ‘Dansarauniya, ya bayyana hakan ne a shafinsa na Facebook a ranar Juma’ar da ta wuce ya na cewa, wasu jagororin bangaren Kwankwasiyya, su na shirin shigowa jam’iyyar APC.
Magaji ya ce, tsaginsu na G7 zai kara yawa a yayin da suke sauraron shigowar wasu manyan ‘yan adawa.
‘Yan G7 su na karkashin jagorancin Malam Ibrahim Shekarau. Daga cikin wadanda za su tsallako zuwa bangaren G7 a cewar tsohon kwamishinan akwai Dr. Yunusa Dangwani, Aliyu Madakin Gini, da kuma Dr. Yusuf Danbatta.