A jiya ne kotun hukunta masu laifukan fyaɗe ta jihar Legas, ta yanke wa wani Fasto mai shekaru 54, Michael Oliseh, hukuncin daurin rai da rai a gidan yari bisa laifin lalata ’ya’yan tagwayen abokinsa ‘yar shekara 12.
Mai shari’a Abiola Soladoye ya samu wanda ake tuhuma da laifuka biyu da suka shafi kazanta da gwamnatin jihar ta gabatar masa.
Oliseh ya aikata laifin ne a wani lokaci a watan Nuwamba 2017 a Ago, kusa da Okota, wani yanki na jihar Legas.
Mai gabatar da kara ya ce, laifukan sun sabawa sashe na 137 na dokokin laifuka na jihar Legas, na shekarar 2015.
A hukuncin da ta yanke, mai shari’ar ta bayyana wanda aka yankewa laifin, wanda ake kira mataimakin limamin cocin Legas a matsayin mai aikata fyaden da ya yi mata fyade, wanda ya rika lalata da ‘ya’yan abokinsa.