fidelitybank

Fursunoni sun tsere daga gidan Yari bayan ƙazamin yaƙi a Congo

Date:

An samu labarin tserewan fursunoni daga wani gidan yari da ke garin Goma a yankin gabashin Jumhuriyar Dimokradiyar Kongo, yayin da rikici ke ƙara ƙamari tsakanin ƴan tawayen M23 da dakarun sojin ƙasar.

Bidiyo da aka wallafa a shafukan intanet sun nuna mutanen da ake kyautata zaton fursunoni ne a titunan birnin, sa’o’i kaɗan bayan da mayaƙan ƙungiyar M23 masu ɗauke da makamai da sojojin Rwanda suka shiga babban birnin lardin Kivu ta Arewa.

Wata majiyar tsaro ta shaidawa kamfanin dilancin labaren AFP cewa an yi tashe-tashen hankula a gidan yari da safiyar ranar Litinin wanda hakan ya yi sanadiyar tserewar fursunonin.

Rahotanni dai na bayyana cewa ƴan tawayen na daf da karɓe iko da Goma da ake cewa sun ƙwace filin saukar jirgin sama.

Gwamnatin Kongo dai ta dage cewa tana samun galaba yayin da ake ci gaba da gwabza faɗa a wasu sassan birnin.

Ana zargin ƙasar Rwanda da marawa ƙungiyar Tutsi ta M23 baya a yayin da take ci gaba kai hare-hare cikin ƴan watannin nan a faɗin yankin mai arzikin ma’adinai.

Rwanda ta sha musanta wannan zargi.

nigeria news today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp