fidelitybank

Fursunoni sun tsere daga gidan Yari bayan ƙazamin yaƙi a Congo

Date:

An samu labarin tserewan fursunoni daga wani gidan yari da ke garin Goma a yankin gabashin Jumhuriyar Dimokradiyar Kongo, yayin da rikici ke ƙara ƙamari tsakanin ƴan tawayen M23 da dakarun sojin ƙasar.

Bidiyo da aka wallafa a shafukan intanet sun nuna mutanen da ake kyautata zaton fursunoni ne a titunan birnin, sa’o’i kaɗan bayan da mayaƙan ƙungiyar M23 masu ɗauke da makamai da sojojin Rwanda suka shiga babban birnin lardin Kivu ta Arewa.

Wata majiyar tsaro ta shaidawa kamfanin dilancin labaren AFP cewa an yi tashe-tashen hankula a gidan yari da safiyar ranar Litinin wanda hakan ya yi sanadiyar tserewar fursunonin.

Rahotanni dai na bayyana cewa ƴan tawayen na daf da karɓe iko da Goma da ake cewa sun ƙwace filin saukar jirgin sama.

Gwamnatin Kongo dai ta dage cewa tana samun galaba yayin da ake ci gaba da gwabza faɗa a wasu sassan birnin.

Ana zargin ƙasar Rwanda da marawa ƙungiyar Tutsi ta M23 baya a yayin da take ci gaba kai hare-hare cikin ƴan watannin nan a faɗin yankin mai arzikin ma’adinai.

Rwanda ta sha musanta wannan zargi.

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...
X whatsapp