fidelitybank

Fursuna ya mutum bayan yajin aikin kin cin abinci na kwanaki 86

Date:

Wani fursuna ɗan ƙasar Falasɗinu ya rasu a gidan yarin Isra’ila sakamakon yajin cin abinci na kwana 86.

Khader Adnan babban ƙusa ne a ƙungiyar masu iƙirarin jihadi, wanda Isra’ila ta zarga da laifukan ta’addanci.

Hukumomin gidan yarin Isra’ila sun ce fursunan ya ƙi amincewa a yi masa magani, kafin a same shi cikin mawuyacin hali a ɗakin da yake ɗaure a gidan yarin ranar Talata.

Firaministan Falasɗinu ya zargi Isra’ila da kisan Adnan ”da gangan” yayin da ƙungiyar masu iƙirarin jihadi ta yi barazanar ɗaukar fansa a kan isra’ila.

Adnan mai shekara 44 – wanda ke zaune a arewacin yamma da gaɓar kogin Jodan – ya kwashe fiye da shekara 20 ana ɗaure shi a gidajen yarin Isra’ila.

Sau huɗu yana shiga yajin cin abinci a baya, lamarin da ya sa sunansa ya yi fice a Falasɗinu.

Yajin cin abinci ga fursunonin Falasɗinu da ke ɗaure a gidajen yarin Isra’ila abu ne da aka saba gani, to sai dai a ‘yan shekarun baya-bayan nan an samu raguwar mace-macensu, sakamakon taimakon magani da aka ba su.

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp