fidelitybank

Fubara ya sake tura wasiƙa ga Ƴan Majalisar jihar kan kasafi

Date:

Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya sake rubuta wa majalisar dokokin jihar wasiƙar sanar da ƴanmajalisar aniyarsa ta sake gabatar da kasafin kuɗin jihar na shekarar 2025, domin neman amincewarsu.

Cikin wasiƙar da gwamnan ya aike wa kakakin majalisar dokokin jihar, Martin Amaewhule ranar Alhamis ya ce yana son gabatar da kasafin a gaban ƴanmajalisar a ranar Laraba 19 ga watan Maris, ko a wata rana cikin watan Maris da majalisar ke ganin zai fi dacewa.

Fubara ya ce matakin biyayya ce ga hukuncin Kotun Ƙolin ƙasar, da kuma buƙatar da ƴanmajalisar suka yi masa na sake gabatar musu kasafin kuɗin jihar.

A cikin wasiƙar gwamnan ya tuna wa kakakin majalisar zuwansa zauren majalisar a ranar Laraba da nufin gabatar da kasafin, amma sai aka kulle ƙofar aka hana shi shiga tare da tawagarsa.

“Za ka iya tuna ziyarar da kawo majalisar a ranar Laraba 12 ga watan Maris domin gabatar da kasafin, domin biyayya ga hukuncin Kotun Ƙoli, amma ba a ba ni damar shiga zauren majalisar ba”, kamar yadda wani ɓangare na wasiƙar ya nuna.

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp