Kungiyar Flying Eagles za ta kara da kulob din Morocco, Kawkab Athletics Marrakesh U-23 a wasan sada zumunta ranar Laraba (yau).
Tawagar Ladan Bosso ta shirya karawa da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ranar Talata amma an soke wasan a minti na karshe.
Wasan sada zumunci da Kawkab Athletics
zai gudana a Complex Sportif, Sidi Mohammed, Ain Sebaa, Casablanca.
Karanta Wannan:Â CAF ta amince da filin wasan da Super Eagles za ta fafata
Za a fara ne da karfe 5 na yamma agogon Najeriya.
Wannan dai shi ne wasan share fage na karshe da kungiyar za ta yi kafin fara kamfen din ta a gasar cin kofin nahiyar Afirka na ‘yan kasa da shekaru 20 ta 2023.
Zakarun gasar sau bakwai za su kara da Senegal a wasansu na farko a filin wasa na Cairo ranar Lahadi.