Kungiyar Flamingos ta samu kyautar kudi naira miliyan uku da kyaftin din Super Eagles Ahmed Musa ya yi wa kungiyar alkawari.
An mikawa ‘yan wasan cekin cekin zuwan su daga Indiya a daren ranar Talata.
Musa ya yi alkawarin bai wa kungiyar kyautar Naira miliyan uku idan ta doke Jamus a karawar da suka yi a matsayi na uku a gasar cin kofin duniya ta mata ‘yan kasa da shekaru 17.
Flamingos sun mika wuya da ci uku-uku a wasan amma daga bisani suka yi nasara da ci 3-2 a bugun fenariti.
Wannan ne karon farko da Flamingos za su karbi lambar yabo a tarihin gasar.
Ana sa ran shugaban kasa Muhammadu Buhari zai karbi bakuncin tawagar nan ba da jimawa ba, sannan kuma za a ba su tukuicin da suka taka rawar gani a kasar Indiya.