fidelitybank

Fiye da mutane 300 na zaman birsun ba tare da an yi musu shari’a ba a Kano

Date:

Kwamitin da babban Sufeton ‘yan Sandan Najeriya ya kafa ya gano cewa akwai fiye da mutum 300 da ke zaman jiran shari’a a wani gidan yarin jihar Kano ba tare da bayanan abubuwan da ake tuhumarsu ba.

Yayin ziyarar ba-zata da kwamitin ya kai ofisoshin ‘yan sanda da kotuna da kuma gidajen yari, ya gano abubuwa da dama da suke buƙatar a sake duba yadda ake tafiyar da su a fannin yadda ake tuhuma da gurfanar da waɗanda ake zargi da aikata wani laifi.

Kwamitin ya fara aiki ne, bayan da shugaban ‘yan sandan ƙasar Mista Kayode Egbetokun ya kaddamar da shirin gyara ayyukan ‘yan sanda a baya-bayan nan, sakamakon kafa wata dokar ‘yan sanda da ake kira ‘Force order number 20’, ta yadda aikin jami’an zai zamo dai-dai da yadda aikin dan sanda abokin kowa ke gudana a duniya.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano CP Hussaini Muhammad Gumel shi ne shugaban kwamtin a Kano, tare da wakilcin ɓangaren shari’a da ‘yan kungiyoyi da lauyoyi da kuma masu rajin kare hakkin dan adam, ya kuma ce sun fara zuwa caji-ofi-din ‘yan sanda ne tun da farko, inda suka gano abubuwa da dama.

Kazalika, CP Hussaini Gumel, yace sun kuma ziyarci kotuna, inda suka tattauna da alkalai da masu gabatar da kara, inda ya cenan gaba za su hadu da mambobin kwamitin, inda za su tattara bayanan da suka samu wuri guda, sannan su fitar da rahoto daya kana a mika wa hukumomin da abin ya shafa don daukar mataki na gaba.

Bayanai na cewa ana-sa-rai, sauran kwamishinonin ‘yan sandan jihohin Najeriya ma, za su bi sahun jihar Kano, wajen gudanar da irin wannan bincike, da nufin gyara yadda aikin ‘yan sanda da bangaren shari’a da gidajen yari suke aiki.

A kwanakin baya ne gwamnatin Najeriya ta kaddamar da shirin rage cunkoso a gidajen yarin Najeriya ta hanyar biya wa masu kananan laifuka tara da yi wa wasu afuwa, sai dai kawo yanzu babu bayanin ko shirin ya ci gaba bayan da aka kaddamar da shi a jihar Kano.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp