fidelitybank

Fiye da mutane 30 ne su ka mutu bayan motar Ɗangote ta aka kan motoci

Date:

Rundunar ƴansandan babban birnin Najeriya Abuja ta tabbatar da mutuwar mutane shida da ƙonewar motoci 14 bayan wata babbar mota ta kama da wuta a yankin Karu.

Kakakin rundunar ƴansandan SP Josephine Adeh wadda ta tabbatar da faruwar lamarin, ta ce ibtila’in ya faru ne a jiya laraba da ƙarfe 6:58 na yamma bayan wata babbar mota da ke maƙare da siminti ta ƙwace ta faɗa kan motocin da ke maƙale cikin cunkoso ababen hawa kusa da gadar Nyanya.

Ta ce ma’aikatan ceto sun yi gaggawar isa wurin da ke cike da baƙin hayaƙi da tsananin zafi domin ceto waɗanda suka maƙale inda ta ce an samu nasarar zaƙulo mutane shida, sai dai bayan kai su asibiti likitoci suka tabbatar da mutuwarsu.

Kakakin rundunar ta kuma ce tare da haɗin gwiwar ƴansanda da ma’aikatan kashe gobara da ma wasu jam’ian tsaro an samu nasarar kashe gobarar.

Rundunar ƴansandan Abuja ta kuma miƙa ta’aziyyarta ga iyalan waɗanda iftila’in ya shafa tare da tabbatarwa da alumma cewa za a gudanar da cikakken bincike kan sanadin iftila’in da kuma yadda za a kare sake afkuwar irinsa.

Sai dai a cewar jami’an VIO, babbar motar kaya ta Kamfanin Dangote mai amfani da iskar gas da ke ɗauke da siminti ta afka kan motoci fiye da 14 kuma ta kashe mutum aƙalla 30 a jiya Laraba a Abuja.

Kwamandan jami’an VIO a yankin Kugbo, Shehu Dalhatu ne ya shaida hakan.

spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp