Rundunar ƴansandan babban birnin Najeriya Abuja ta tabbatar da mutuwar mutane shida da ƙonewar motoci 14 bayan wata babbar mota ta kama da wuta a yankin Karu.
Kakakin rundunar ƴansandan SP Josephine Adeh wadda ta tabbatar da faruwar lamarin, ta ce ibtila’in ya faru ne a jiya laraba da ƙarfe 6:58 na yamma bayan wata babbar mota da ke maƙare da siminti ta ƙwace ta faɗa kan motocin da ke maƙale cikin cunkoso ababen hawa kusa da gadar Nyanya.
Ta ce ma’aikatan ceto sun yi gaggawar isa wurin da ke cike da baƙin hayaƙi da tsananin zafi domin ceto waɗanda suka maƙale inda ta ce an samu nasarar zaƙulo mutane shida, sai dai bayan kai su asibiti likitoci suka tabbatar da mutuwarsu.
Kakakin rundunar ta kuma ce tare da haɗin gwiwar ƴansanda da ma’aikatan kashe gobara da ma wasu jam’ian tsaro an samu nasarar kashe gobarar.
Rundunar ƴansandan Abuja ta kuma miƙa ta’aziyyarta ga iyalan waɗanda iftila’in ya shafa tare da tabbatarwa da alumma cewa za a gudanar da cikakken bincike kan sanadin iftila’in da kuma yadda za a kare sake afkuwar irinsa.
Sai dai a cewar jami’an VIO, babbar motar kaya ta Kamfanin Dangote mai amfani da iskar gas da ke ɗauke da siminti ta afka kan motoci fiye da 14 kuma ta kashe mutum aƙalla 30 a jiya Laraba a Abuja.
Kwamandan jami’an VIO a yankin Kugbo, Shehu Dalhatu ne ya shaida hakan.